Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yaba wa Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, bisa jajircewarsa wadda ya ce ita ce silar nasarorin da jam’iyyar APC ta samu a zaɓen da aka gudanar a Abuja.
A ranar Asabar ce Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC ta gudanar da zaɓe a ƙananan hukumomi shida na Babban Birnin Tarayya, tare da zaɓukan cike gurbi a mazaɓun Ahoada East II da Khana II a Jihar Ribas, da kuma Kano Municipal da Ungogo a Jihar Kano.
