Daga Mustapha Abdullahi Abubakar
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda, ya taya Ibrahim Masari murna bisa karin girman mukamin da aka yi masa zuwa matsayin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Siyasa daga hannun Shugaban Ƙasa Bola Tinubu.
An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan, Ibrahim Kaula, ya fitar kuma ya rabawa manema labarai a yau Juma’a.
Radda ya bayyana cewa wannan naɗin mukami alama ce karara da ke nuna cewa Tinubu ya fahimci muhimmanci da jajircewar ɗan siyasar da ya fito daga Jihar Katsina.
Gwamnan ya ce:
“Wannan karin girman shaida ce ta jajircewa da ƙwazon aiki na Masari.
Shugaban ƙasa ya nuna cewa yana daraja aminci, ƙwarewa, da basirar siyasa.
Gwamnan ya kuma lura cewa wannan naɗin ya zo ne a wani muhimmin lokaci da ƙasar ke buƙatar ƙwararrun mutane domin taimakawa wajen ciyar da manufofin siyasar shugaban ƙasa gaba.
Karanta:Bauchi Launches SightQuest Programme To Combat Preventable Blindness
Radda ya ƙara da cewa wannan karin girman mukami yana nuna irin amincewar da Tinubu ya dade yana da ita ga Masari tun daga farko.
A ƙarshe, Radda ya nuna godiya ga Shugaba Tinubu, tare da bayyana kwarin gwiwarsa cewa sabon mukamin na Masari zai amfanar da gwamnatin tarayya, har ma da Jihar Katsina da yankin Arewa maso Yamma baki ɗaya.
Recent:An kori mutane 22 a Jigawa sakamakon badakalar ciyarwar a watan Ramadan.
