Majalisar Wakilai a Nijeriya ta ce ta fara duba dokokin gyaran haraji bayan korafe-korafen jama’a da zargin an sauya wasu sassan dokokin da aka riga aka wallafa a sanarwar da gwamnati ta ba jama’a.
Mai magana da yawun Majalisar Akin Rotimi, ya ce an kafa kwamitin da zai binciki yadda aka bi wajen tsara wa da kuma aiwatar da dokokin domin gano ko akwai kura-kurai, tangarɗa ko wani tsoma baki a tsarin majalisa da na gudanarwa.
Gidan talabijin na Channels ya ruwaito Rotimi ya ƙara da cewa Majalisar ta umarci Akawun Majalisar a sake wallafa dokokin tare da fitar da sahihan kwafi-kwafi na abin da Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai suka amince da shi.
Ya kuke kallon wannan sabon matakin?
