Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin cewa Najeriya za ta murƙushe ta’addanci, bayan wani mummunan harin Boko Haram a Jihar Borno State wanda ya yi sanadin mutuwar Birgediya Janar Oseni Omoh Braimah da wasu sojoji da dama.
Da yake mayar da martani kan harin da aka kai wa sansanin soji a Benisheikh, Tinubu ya ce harin alama ce ta rashin mafita daga ‘yan ta’adda da ke fuskantar matsin lamba mai tsanani daga sojojin Najeriya. Yayin da yake alhinin rasuwar sojojin, Tinubu ya bukaci shugabannin rundunar sojoji da dukkan sojojin da ke kan gaba da kada su karaya, sai dai su samu ƙwarin gwiwa daga irin gagarumar godiyar da ƙasa ke yi wa sadaukarwar da suke yi.
karanta:A Tattauna Da Boko Haram Don Sako Mana Mutane 416 Da Aka Kama – Ƙungiya A Borno.
Tinubu ya ce rundunar sojojin Najeriya na ci gaba da kai hare-hare masu ƙarfi ta ƙasa da sama, inda ake hallaka mayaƙa da kwamandojinsu da dama, sannan ya ƙara da cewa hare-haren baya-bayan nan na nuna cewa ‘yan ta’adda na fama da wahala wajen tinkarar cigaban da sojoji ke samu.
Recent:Filato: Mutane 8 Sun Mutu, Wasu Sun Jikkata a Harin Bokkos.
